Header Ads Widget

Responsive Advertisement

Sakon ta'aziyya ga Gwamnan jihar Katsina



Shugaban kamfanin jaridar yanar Gizo mai suna ( HAUSA MEDIA REPORTERS) tare ma'aikatanta baki ɗaya na miƙa sakon ta’aziyya da juyayi ga mai Girma Gwamnan Jihar Katsina, Malam Dikko Umar Radda, bi sa rasuwar mahaifiyarsa 

A cikin saƙon ta'aziyyar,  shugaban ya ayyana cewa, rashin da iyalan gwamnan sukai babban rashi ne da ya shafi ɗaukacin al’ummar Jihar Katsina da Najeriya gaba ɗaya.

Shugaban  yayi rokon Allah Maɗaukakin Sarki ya gafarta ma ta da Rahama, Ubangiji  ya sanya ta cikin Aljanna Firdausi.

Post a Comment

0 Comments