Header Ads Widget

Responsive Advertisement

Mai Girma Malam Umar Namadi, Gwamnan Jihar Jigawa, ya halarci Taron Kasuwanci na Najeriya da kasar Masar


Mai Girma Malam Umar Namadi, Gwamnan Jihar Jigawa, ya halarci Taron Kasuwanci na Najeriya da kasar Masar wanda aka gudanar a hotal din Transcorp Hilton, Abuja.

A wajen taron, Gwamna Namadi ya gayyaci masu zuba jari daga Masar da su ziyarci jihar Jigawa domin gani da idon su dimbin damar zuba jari da ke akwai a jihar, tare da haskaka manufofin jihar na saukaka harkokin kasuwanci, ci gaban ababen more rayuwa da kuma albarkatun noma.

Halartar gwamnan a wannan taro na nuna jajircewar Jihar Jigawa wajen karfafa hadin gwiwar kasa da kasa domin bunkasa tattalin arziki, samar da ayyukan yi, da inganta rayuwar al’umma.

Post a Comment

0 Comments