MEKE FARUWA A HUKUMAR RIVER BASIN?
Daga Umar Idris, Zariya
Shin me ake nufi da Hukumar Raya Kogin (River Basin Development Authority - RBDA)?
Hukumace ta raya Kogi hukuma ce da gwamnati ke kafa wa don kula da bunkasa albarkatun ruwa a wani yanki na kogin ko tafkin ruwa. Ayyukan da irin wannan hukuma ke yi sun hada da:
Noma ban ruwa da ci gaban aikin gona
Kula da ambaliya da adana ruwa
Ci gaban yankunan karkara da bayar da goyon baya
Samar da wutar lantarki daga ruwa (hydropower)
Kula da koguna da dasa itatuwa a dazuka (reforestation)
Misalai:
Najeriya: A Najeriya akwai hukumomi da dama irin su Hukumar Raya Kogin Sokoto-Rima da Hukumar Raya Kogin Lower Niger, wadanda ke aiki don bunkasa aikin noma, kula da ruwa, da tallafawa tattalin arzikin al’umma
Bisa haka ne Majalisar Shugabannin Jam’iyyu na Siyasa a Najeriya (CPPCN) ta bayyana damuwarta kan yadda aka sauya sunan wanda aka gabatar domin nada shi Shugaban Hukumar Raya Karkara ta Kasa (River Basin Development Authority), inda ta bukaci a gudanar da gaggawar bincike da kuma sake duba lamarin cikin adalci da gaskiya.
Majalisar ta yaba da irin kokarin da Shugaban Kasa, Bola Ahmed Tinubu ke yi wajen karfafa hukumomin gwamnati ta hanyar nade-naden da ke da manufar inganta gudanarwa da ci gaban kasa.
Rashin Bin Ka’ida
Sai dai CPPCN ta bayyana cewa nada Aliyu Tajudeen — dan uwan Kakakin Majalisar Wakilai Rt. Hon. Tajudeen Abbas — a matsayin Darakta-Janar ya bar baya da kura, ganin cewa an gabatar da Hon. Shuaibu Bawa Jaja a matsayin zabin Gwamna Malam Uba Sani, kuma an ruwaito cewa shugaban kasa ya amince da shi.
Hon. Jaja, wanda ya taba rike mukamin Shugaban Karamar Hukumar Kudan da kuma Shugaban ALGON a Kaduna, yana da dogon tarihi a fagen siyasa da jajircewa, musamman a lokacin zaben 2023.
Majalisar ta ce rashin bayyana dalilin da yasa aka canza wanda aka amince da shi zuwa wani dan uwan wani babban jami’in gwamnati, tamkar take dokar cancanta ne da gurgunta tsarin dimokradiyya.
Batutuwan Da Suka Janyo Cece-kuce:
Nada ‘yan uwa da abokan arziki a manyan mukamai ba tare da la’akari da cancanta ba yana janyo koma baya a siyasance.
Take Darajar Ofisoshin Gwamnati: Watsi da zabin gwamna na nuna rashin daraja ga gwamnoni da kuma wadanda suka sadaukar da kansu wa jam’iyya.
Rashin Gaskiya: Babu wani bayani daga bangaren gwamnati kan yadda aka sauya sunan wanda aka gabatar da farko.
Shawarwarin CPPCN:
1. Shugaba Tinubu ya sake duba wannan nade-nade tare da tabbatar da gaskiya da adalci.
2. Gwamna Uba Sani ya tsaya tsayin daka wajen kare zabinsa da martabar ofishinsa.
3. A gudanar da bincike mai zaman kansa domin gano hakikanin abin da ya faru.
4. Rt. Hon. Tajudeen Abbas ya nisanta kansa daga zargin amfani da mukaminsa domin amfanar da ‘yan uwa.
Kammalawa:
“Majalisar CPPCN za ta ci gaba da kare tsarin dimokradiyya, saka wa wadanda suka sadaukar da kai, da tabbatar da cewa duk nade-nade suna wakiltar muradun jama’a gaba daya,” in ji sanarwar.
0 Comments