Farfesa Adamu Abubakar Gwarzo Ya Bada Tallafin Bas Mai Kujeru 60 Ga Jami'ar FUDMA
Jami’ar Tarayya ta Dutsin-Ma (FUDMA) ta gudanar da taron yaye Éalibai a karo na 9, a inda ta samu wani karamcin kyauta ta musamman daga Farfesa Adamu Abubakar Gwarzo, a inda ya bai wa jami’ar motar bas mai cin mutum 60.
Sabuwar motar bas Éin za ta sauĘaĘa Ęalubalen sufuri ga Éalibai, waÉanda da yawa daga cikinsu ke kokawa bisa Ęarancin motocin zirga-zirga.
A yayin bikin, shugaban jami'ar ta FUDMA, Farfesa Armaya'u Bichi, ya bayyana matuĘar jin daÉin jami'ar ga irin gudunmawar da Farfesa Gwarzo ya bayar.
"Wannan motar bas Éin za ta zama babbar Ęadara ga Éalibanmu, tare da Ęarfafa su wajen halartar azuzuwa da kuma shiga cikin harkokin karatu," in ji Farfesa Bichi.
"Muna matuĘar godiya da jajircewar Farfesa Gwarzo na tallafawa ilimi a aikace ta hanyoyi masu tasiri.
Ęalibai da ma'aikatan da suka halarci taron sun yi nuna jinÉaÉin su bisa yadda wannan kyautar sabuwar motar bas za ta yi tasiri ga rayuwar su ta tau da kullum a harabar jami'a.
Karamcin na Farfesa Gwarzo abin koyi ne kuma tunatarwa ne mai tasiri ga yadda tallafin zai iya haÉaka ilimi da ba da gudummawa ga nasarar Éalibai.
0 Comments