Header Ads Widget

Responsive Advertisement

Jami'an Karota Ne Ke Bayar Da Tsaro A Zaɓen Ƙananan Hukumomin Kano


Jami'an hukumar kiyaye dokokin tuƙa ababen hawa ta jihar Kano KAROTA, ne ke samar da tsaro a rumfunan zaɓen ƙananan hukumomin jihar.

Tun da fako dama rundunar 'yansandan jihar ta ce ba za ta shiga zaɓen ba, bisa umarnin kotun tarayya da ta buƙaci kada su shiga cikin wani hukunci da ta yanke cikin makon nan, kodayake babbar kotun jihar ta bayar da wani hukuncin da ya ce jami'an 'yansandan su shiga zaɓen.

A yanzu dai jami'an KAROTA na 'yan Vigilante ne ke bayar da tsaro alokacin zaɓen.

Kuma kawo yanzu babu labarin wani tashin hankali ko hayaniya.

Post a Comment

0 Comments